Hadisai daga Imam Ali (as) Hadisai daga Imam Ali (as) 1-Imam Ali[AS] ya ce, “ Duk wanda ya gyara tsakaninsa da Allah to Allah zai gyara tsakaninsa da mutane,duk wanda ya gyara al’amarin lahirarsa to Allah zai gyara al’amarin duniyarsa.” 2- Imam Ali[AS] ya ce, “ Ya kai ]an Adam idan ka ga Allah Ta’ala yana yi maka ni’imomi alhali kana saba masa to ka yi hankali.” Wato zai kasance kenan istidraji ga mutum. 3- Imam Ali[AS] ya ce, “ Idan ka samu iko kan ma}iyinka ka yi afuwa gareshi a matsayin godiya ga Allah kan wannan iko da ka samu akansa. 4-Imam Ali[AS] ya ce, “Mutane basu bar wani abu ba na al’amarin Addininsu saboda mas’lahar duniyarsu face Allah Ta’ala ya bude masu abunda ya fi haka tsanani.” 5- Imam Ali[AS] ya ce, “Duk wanda yasa kansa a in da za a iya tuhumarsa,to ka da ya zargi duk wanda ya munana masa zato.”misali mutum ...